MARYAMA DASSHIYA
Da sunan Allah maƙagin halitta,         Mai rayawa mai kashe halitta,
Salati ga Muhammadu ɗan gata,         Wanda ba shi fushi sai yawan kyauta,
Alaye da sahabatiduk abin yabawa.

Sun ce waqa ta Hausa bani iyawa,    Ni ko nac ce musu waƙa gare ni baiwa,
Don cikin hikima ɗai taka tsaruwa,  Layuka zuwa ɗango sannan rerawa,
Gashi ko yau sun yi tsit ba tankawa.

Yaku zo waƙa ce za na yo ta,               Can cikin zuciya ne an ka tsara ta,
Manufa dai yabo cikin soyayyarta,   Wacce ganinta ke sace nutsuwata,
In zam fili da baɗili abin makancewa.

Maryama kenan dasasshiya,              Ɗaya tamkar uku babu jayayya,
Kainuwa kike wane aikin kishiya,     Hasken silba, ki ɗau ido, ki ɗau zuciya,
Farar  auduga mai yawan murmusawa.

Zo ka ga tsurar kyawu gun Indiyana,    Fararan idonu ga hanci miƙe Indiyana,
Cif-cif take gun fasali nata Indiyana,    Ka ji zamani kowa dole ya yi ki Indiyana,
Sannan gare ki kallo ne da sallamawa.

Ko cikin qur’ani akwai sunanki,       Cikin sutura kamila abinki,
Kowa shaida ne babu ruwan ki,        Son kowa, ana rububin ki,
Sai ta ce; “Anas, ni kai nake yabawa”.

Layuka arba’in raunana suke,           Cikin baitoci takwas suke,
Saidai ba su iya misalta yaya kike,   Kai ko numfashi da ke jikina ƙaƙa yake,
Duk tsawon zamanina ba ki iya kwatantuwa.

Alhamdulillah ga ubangijin rayuka,     Gani durƙushe a fadarka,
Wannan ta rahma ga bayi duka,            Roƙon alkhairi muke gare ka,
Allahu ka ba mu soyayyar sanyayawa…….!

Rubutawa;
(c) Anas Ɗansalma

Popular posts from this blog

Every day humbles me

YADDA ZA KA YI AMFANI DA HARUFAN "ƙ da ɓ da ƴ ('y)" DOMIN YIN INGANTACCEN RUBUTU NA HAUSA A KWAMFUTA DA WAYAR HANNU